Wata mata ta bayyana yadda ƴan bindiga suka yiwa gidan su a Abuja ƙawanya suka sace iyalin ta
Wata mata da abin ya rutsa da ita mai suna Misis Janet ta bayyana yadda wasu ‘yan bindiga suka kai farmaki gidanta da ke unguwar Kwali a Abuja suka yi awon gaba da iyalanta baki daya. Da take magana a gidan talabijin na AIT, Janet ta bayyana abin da ta gani a kofar gidanta yayin da maharan suka jagoranci iyalanta suka fita daga gidan.
Da take ba da labarinta, wadda abin ya shafe ta ce, “Muna barci da misalin karfe 12 na dare, sai karen mu ya fara ihu da karfi.” Mun cigaba da lekawa ta tagogin mu kawai dai muka gano cewa an kewaye katangar mu. Muna kallon yadda masu garkuwar suka yi tsalle suka shiga harabar gidan, sai na gaya wa mijina cewa lokacin mu ne. Suna kokawa da kofar mu, amma na bijirewa mijina ta hanyar bude musu kofa. Na roke su na ce zan bude musu kofa. Da bude kofa, sai aka tura mu kasa, kuma an kusa kaiwa mijina hari da yankan katako, amma ya roki su.
Ta cigaba da cewa, “An umarce mu da mu mika musu kudin mu da wayoyin mu, amma sai suka cigaba da tura mu waje yayin da suka kai mu bakin gate. Mun hadu da mutane da yawa masu rike da bindigogi a kofar gidan mu, sai daya daga cikin su ya bugi kan mijina da sandar makiyaya, aka daure shi. Sun yi ta harbe-harbe sa’ad da suke garkuwa da mu, kuma suka yi ta bugun bayana da sanda. An kai mu cikin daji inda suka yanke shawarar saki na da wayata don mu tafi gida in samo kudin fansa Naira miliyan 10 bayan na yi alkawarin gwadawa. Na yi nasarar komawa gida a daren nan ta cikin ciyayi. Sai dai tun daga lokacin sun kara kudin fansa zuwa Naira miliyan 17.
Sace dangin Janet ya kai ga rufe FGC Kwali a Abuja. Za ku iya tunawa cewa hare-haren da wasu da ake kyautata zaton ‘yan ta’adda ne suka kai a Abuja a baya-bayan nan ya tayar da hankalin ‘yan Najeriya.